Mataimakin kwamishinan yan sandan jihar Borno ya mutu a hatsarin mota

Rundunar ƴan sandan jihar Borno ta sanar da mutuwar , Abubakar A. Balteh mataimakin kwamishinan yan sanda na jihar wanda ya mutu a ranar Asabar sakamakon wani mummunan hatsarin mota.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, ASP Nahum Kenneth Daso ne ya bayyana haka a cikin wani sako da ya wallafa a shafin sa na X .

Nahum ya bayyana rasuwar Balteh a matsayin wani babban rashi mai ciwo ga rundunar yan sandan Najeriya da kuma rundunar yan sandan jihar Borno.

Kafin rasuwar marigayin shi ne  ke rikon muƙamin shugaban sashen binciken manyan laifuka na rundunar yan sandan jihar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]