Masu zanga-zanga sun yi galaba kan soja a Sudan

Zanga-zangar Sudan

Wasu jiga-jigan gwamnatin mulkin soja su uku a Sudan sun mika tayin sauka daga kan mukamansu- wata muhimmiyar bukata ce ta masu zanga-zanga a kasar.

Ana kallon manyan janar-janar din a matsayin manyan na-hannun daman tsohon shugaba Omar al-Bashir.

Matakin ya zo ne bayan tattaunawa tsakanin sojoji da jam’iyyun adawa kan yadda za a kafa gwamnatin farar hula.

A wani taron manema labarai, kakakin rundunar sojan kasar Laftanar Janar Shamseddine Kabbashi ya ce bangarorin biyu sun cimma matsaya kan mafi yawan bukatun kuma sun yanke shawarar kafa kwamitin hadin gwiwa don warware duk wasu matsaloli.

Jagororin zanga-zanga a Sudan din sun kira wani maci na mutum miliyan daya a yau Alhamis domin matsawa majalisar koli ta sojan kasar mika mulki ga gwamnatin farar hulla.

Jiragen kasa makare da mutane na isa Khartoum, babban birnin kasar don shiga gangamin da za a yi a wajen shelkwatar rundunar soji.

A karon farko, alkalai sun bayyana cewa za su shiga zanga-zangar don nuna goyon bayansu, a cewar kamfanin dillancin labarai na AFP.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...