Maman Taraba ta nemi addu’ar yan Najeriya kan aikin tiyata da za ayi mata

Toshuwar ministar harakokin mata Hajiya Aisha Jummai Alhassan wadda aka fi sani da Mama Taraba ta nemi yan Najeriya da suyi mata addu’a kan aikin tiyata da za a yi mata a kokon gwiwarta.

Alhassan ta fadi rokon nata ne cikin wani gajeren sako da ta wallafa a shafinta na Twitter.

“Na shirya domin yimin aikin tiyatar sauya kokon gwiwa.Dan Allah ina bukatar kuyi muni addu’a. Allah ya ƙaddara saduwar mu,Amin,”a cewar sakon da ta wallafa.

Shekarar da ta gabata dai an ta rade-radin tsohuwar ministar bata da lafiya bayan da aka shafe watanni ba a ganinta a bayyanar jama’a.

Daga bisani Alhassan tayi karin haske kan cewa ta kwanta biyar wani ciwo da ta bayyana ba.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...