Malamin addinin Muslunci ya shiga hannun DSS bayan sukar gwamnatin Buhari

Ana zargin hukumar tsaro ta farin kaya, wadda aka fi sani da DSS, da tsare wani malamin addinin Musulunci mazaunin jihar Katsina mai suna Abu Ammar.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa an kama shine ranar Talata kan wata huduba da ya yi inda a ciki ya zargi gwamnatin shugaban kasa Muhammad Buhari da yin ko in kula kan yadda sha’anin tsaro ya tabarbare a sassa daban-daban na kasarnan.

Wakilin jaridar Daily Trust ya gano cewa,Abu Ammar na tare da abokinsa mai suna Mallam Shamsu lokacin da aka kira shi a waya aka bukaci da ya kai kansa ofishin hukumar DSS na jihar.

Malamin ya amsa gayyatar inda suka tafi tare da Shamsu zuwa ofishin amma daga bisani sai suka ce abokin nasa ya dawo gida shi kuma suka cigaba da tsare shi.

Murtala É—a ne ga malamin ya tabbatarwa da wakilin jaridar tsare mahaifinsa lokacin da wakilin ya ziyarci gidansu dake Filin Samji a Katsina.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]