Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya gode wa Shugaba Bola Tinubu da jami’an tsaro bisa nasarar ceto ɗalibai da malamai da aka sace a ƙaramar hukumar Oriire.
An kuɓutar da mutanen ne bayan sun shafe kwanaki 56 a hannun masu garkuwa da mutane. Sojoji, jami’an DSS da ‘yan sanda ne suka gudanar da aikin ceton.
Makinde ya bayyana cewa ceton ya kawo babban sauƙi ga gwamnati da iyalan waɗanda abin ya shafa. Ya kuma gode wa Shugaba Tinubu da dukkan jami’an tsaro saboda ƙoƙarin da suka yi.
Shi ma Shugaba Tinubu ya yaba da aikin jami’an tsaron. Ya ce za a ba waɗanda aka ceto kulawar lafiya da sauran tallafi. Haka kuma, ya yi alƙawarin tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa da kuma iyalan malamin da aka kashe a lokacin satar.
Makinde Ya Gode Wa Tinubu Da Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai Da Malama a Oyo

