Majalisar dattawa ta amince Tinubu ya kori wasu kwamishinonin zaɓe 3

Majalisar dattawa ta amince da buƙatar shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu da ya mika mata ta neman korar dakatattun kwamshinonin zaɓen jihohin Adamawa, Sokoto da kuma Abia.

An amince da bukatar shugaban ƙasar ne bayan da Opeyemi Bamidele shugaban masu rinjaye na majalisar ya gabatar kudiri kan batun a ranar Laraba.

Kwamishinonin su ne Ike Uzochukwu, (Abia), Hudu Yunusa-Ari, (Adamawa), da kuma Nura Ali (Sokoto).

Tinubu ya nemi amincewar majalisar ne na kawo ƙarshen aikin kwamishinonin ne kan aikata ba dai-dai.

Da yake gabatar da kudirin, Bamidele ya ce buƙatar shugaban ƙasar ta yi dai-dai da sashe na 157(1) na kundin tsarin mulkin Najeriya.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan batun, Abba Moro shugaban marasa rinjaye ya ce korar ta su za ta zama izina ga waɗanda suke riƙe da mukamin gwamnati.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]