Lagos: Mutane biyar sun halaka a hatsarin jirgin kasa

Wani jirgin kasa dake kan hanyarsa ta zuwa jihar Ogun ya bi ta kan mutane biyar ciki har da wani matukin babura mai kafa uku bayan da babur din ya hau kan digar jirgin.

Jirgin dake dauke da fasinjoji ya ci karo ne da babur din me kafa uku abun da ya jawo mutuwar dukkanin fasinjoji dake ciki.

Jaridar Daily Trust ta gano cewa jirgin ya taso daga tashar Ike Aro a jihar Lagos inda ya nufi tashar Itoki dake jihar Ogun lokacin da mummunan hatsarin ya faru.

A cewar shedun ganin da ido lokacin da jirgin ya doso motoci da kuma masu tafiya a kasa dukkansu sun dakata domin bawa jirgin damar wucewa.

Amma matukin babur din ya yi kokarin tsallakawa abin da ya jawo jirgin ya nuke su tare da fasinjojin dake ciki.

More News

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ćłan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...

Hukumar NDLEA ta lalata sama da tan 300 na miyagun kwayoyi da aka kama a Legas da Ogun

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta yi nasarar lalata kilogiram 304,436 da lita 40,042 na haramtattun abubuwa da...