Wani jirgin kasa dake kan hanyarsa ta zuwa jihar Ogun ya bi ta kan mutane biyar ciki har da wani matukin babura mai kafa uku bayan da babur din ya hau kan digar jirgin.
Jirgin dake dauke da fasinjoji ya ci karo ne da babur din me kafa uku abun da ya jawo mutuwar dukkanin fasinjoji dake ciki.
Jaridar Daily Trust ta gano cewa jirgin ya taso daga tashar Ike Aro a jihar Lagos inda ya nufi tashar Itoki dake jihar Ogun lokacin da mummunan hatsarin ya faru.
A cewar shedun ganin da ido lokacin da jirgin ya doso motoci da kuma masu tafiya a kasa dukkansu sun dakata domin bawa jirgin damar wucewa.
Amma matukin babur din ya yi kokarin tsallakawa abin da ya jawo jirgin ya nuke su tare da fasinjojin dake ciki.