Kwastam sun kama kwantenoni 34 dauke da shinkafar da ta lalace – AREWA News

Hukumar Custom ta ce jami’anta sun kama kwantenoni 34 makare da lalatacciyar shinkafa da aka yi fasa kaurinsu zuwa tashar jiragen ruwa ta Tin Can Island dake Legas daga kasashen Thailand da China.

Shugaban hukumar, Hamid Ali shine ya sanar da haka ranar Talata, ya ce wasu daga cikin buhunan shinkafar wa’adin amfani da su ya kare yayin da wasu kuma suke dab da karewa.

Kama kwantenonin na zuwa ne kwanaki hudu bayan da hukumar ta kama kwantenoni 25 makare da kayan abinci da wa’adinsu ya kare duk a tashar jirgin kuma kwana daya bayan da aka gano wasu kwantenoni hudu makare da kifi da ya fara rubewa a yankin Apapa dake jihar.

Ali ya ce hukumar ta kuma kwace kwantena 11 dauke da magunguna da ba ayi musu rijista, kwantenoni biyu ta tsofaffin tayar mota,kwantena daya ta kayan gwanjo da kuma kwantenoni hudu na man girki.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...