Kudurin kawo karshen almajiranci a Najeriya ya janyo ka-ce-na-ce

Babagana Mungono, mai ba shugaban kasa shawara akan harkokin tsaro, ya sanar wa manema labarai wannan batu na kawo karshen almajiranci jim kadan bayan kammala wani babban taro a birnin tarayya Abuja ranar Alhamis 20 ga watan Yuni.

Wannan lamari ya ja hankalin majalisar kula da malaman makarantun allo a jihar Kaduna dake gani matakin da ake shirin dauka bai dace ba.

Imam Buhari Maraban Jos, sakataren majalisar malaman makarantun allo a jihar Kaduna, ya ce sun yi mamakin jin wannan sanarwar akan almajirai daga mutumin da ya fito daga Maiduguri. Ya kuma ce kamata yayi idan an hango wata matsala a zauna da shugabannin kungiyarsu ta kasa a ga yadda za a magance matsalar.

Imam Buhari, ya kuma ce mafi yawan wadanda ake gani akan titi suna bara, ba almajirai bane, rashin shugabanci na gari ne ya haifar da wannan matsalar har wasu ke amfani da rigar almajirai su na bara.

Shi kuma mai taimakawa gwamnan jihar Kaduna akan harkokin addinin musulunci Sheikh Jamilu Abubakar Albani, ya ce ko da yake akwai kurakurai game da almajiranci a Najeriya, bai kamata a yanke wannan hukuncin ba tare da an tattauna da malaman dake wannan harka ba, a ji yadda suke gani ya fi dacewa a magance matsalar.

Masanin harkokin tsaro Manjo Yahaya Shinko mai ritaya, shi kuma ya ce a ganin sa, rashin tsaro bai da alaka da almajiranci amma dai da bukatar a gyara batun karatun Muhammadiyya a kasar.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...