Kotu ta tabbatar wa da Simon Lalong na Filato nasara | BBC Hausa

Simon Lalong

Hakkin mallakar hoto
Gwamnatin jihar Filato

Alkalan kotun koli sun kori karar dan takarar gwamnan jam’iyyar PDP na jihar Filato, Jeremiah Useni, inda kotu ta tabbatar da Simon Lalong na jam’iyyar APC a matsayin mutumin da ya lashe zaben 2019.

Sakamakon zaben zagaye na biyu da aka yi a ranar 26 ga watan Maris din 2019 ya nuna Gwamna Lalong ya kayar da tsohon ministan Abuja Jeremiah Useni na jam’iyyar PDP.

An gudanar da zaben ne a mazabun kananan hukumomi tara wadanda ba a kammala ba a zaben farko na gwamna da aka gudanar a ranar 9 ga Maris.

Jam’iyyar APC ta lashe kananan hukumomi shida a mazabun da aka sake zaben. Jam’iyyar PDP kuma ta lashe kananan hukumomi uku.

Yanzu APC ta lashe kananan hukumomi 11 cikin 17 na jihar Filato yayin da PDP ta lashe kananan hukumomi guda shida.

Filato na cikin jihohin da suka ja hankali ake karasa zabukan gwamnoni wadanda suka hada da Bauchi da Benue da Kano da kuma Sokoto.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...