Jirgin kasa ya kashe wasu mutane biyu a Kano

Ƴansanda a jihar Kano a ranar Talata sun tabbatar da mutuwar mutane biyu wadanda jirgin kasa ya markade su har lahira.

DSP Abdullahi Haruna mai magana da yawun rundunar yansandan jihar shine ya tabbatar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar.

Haruna ya ce “Ranar 16 ga watan Afirilu da misalin karfe 8 na safe mun samu rahoton cewa wasu mutane da ba a gane ko suwaye ba dake kwance akan digar jirgi kasa, jirgin ya talutse su har lahira a bayan Kano Club dake karamar hukumar Nasarawa ta jihar.”

A cewarsa lokacin da yansanda suka isa wurin da lamarin ya faru sun gano cewa daya daga cikin mamatan jirgin ya datsa shi gida biyu.

Mai magana da yawun rundunar ya yi kira ga jama’a da su kaucewa digar jirgi domin gudun faruwar hatsari makamancin wannan.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...