
Wani tsagi na jam’iyar SDP ya zaɓi Sadik Gombe a matsayin halastaccen shugaban jam’iyar na ƙasa.
Kafin zaɓen nasa, Gombe ya kasance shugaban riƙo na jam’iyar tun shekarar 2025 kafin zaɓen da aka yi masa a lokacin babban taron jam’iyar da aka gudanar a filin wasa na Tafawa Balewa dake Bauchi.
Jam’iyar ta kuma zabi sauran shugabanni da suka haɗa da Ugochukwu Uba (mataimakin shugaban jam’iyar shiyar Kudu ), Olu Agunloye (sakatare), Mariam Batubo (ma’aji ), Joseph Abu (sakataren tsare-tsare na kasa), Araba Aiyenigba (mai magana da yawun jam’iyar), Aderemi Abimbola (mai bada shawara kan harkokin sharia), Bello Hussaini (sakataren kuɗi), Sa’adatu Abdullahi (shugabar mata), da kuma Daniel Ibe (shugaban matasa).
Da yake jawabi bayan kammala zaɓen, Gombe ya ce SDP za ta samar da bigiren da ake buƙata na ceto Najeriya daga mawuyacin halin da ta ke ciki.

