Hukumomin Ƙasar Masar Sun Bawa Daliban Najeriya Damar Shiga Kasar Daga Sudan

Abike Dabiri-Erewa shugaban hukumar NIDCOM dake lura da yan Najeriya mazauna kasashen waje ta ce gwamnatin Misra ta buɗe kan iyakarta ga ɗaliban Najeriya da aka dauko daga Sudan.

Dabiri-Erewa ta ce an buɗe kan iyakar ne biyo bayan wayar tarho da shugaban kasa Muhammad Buhari ya yi da takwaransa na Masar, Abdulfatah El-Sisi.

Sanarwar ta NIDCOM na zuwa ne sa’o’i bayan sanarwar da hukumar ta fitar dake cewa hukumomin ƙasar Masar sun gaza buɗe kan iyakar duk da cewa jiragen rundunar sojan saman Najeriya sun isa kasar domin kwato ɗaliban.

Ta kara da cewa an bude kan iyakar ne bayan gindaya wasu tsauraran sharuɗa da bata bayyana ba.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]