Abike Dabiri-Erewa shugaban hukumar NIDCOM dake lura da yan Najeriya mazauna kasashen waje ta ce gwamnatin Misra ta buÉ—e kan iyakarta ga É—aliban Najeriya da aka dauko daga Sudan.
Dabiri-Erewa ta ce an buÉ—e kan iyakar ne biyo bayan wayar tarho da shugaban kasa Muhammad Buhari ya yi da takwaransa na Masar, Abdulfatah El-Sisi.
Sanarwar ta NIDCOM na zuwa ne sa’o’i bayan sanarwar da hukumar ta fitar dake cewa hukumomin Æ™asar Masar sun gaza buÉ—e kan iyakar duk da cewa jiragen rundunar sojan saman Najeriya sun isa kasar domin kwato É—aliban.
Ta kara da cewa an bude kan iyakar ne bayan gindaya wasu tsauraran sharuÉ—a da bata bayyana ba.