Hukumar Yaƙi da Masu Karya Tattalin Arziki ta EFCC ta bayar da sanarwar neman tsohuwar Ministar Jinƙai da Harkokin Agaji, Sadiya Umar Farouq, ruwa a jallo.
A wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta ce ana neman tsohuwar Ministar ne domin ta fuskanci shari’ar da ta shafi zargin badaƙalar kuɗaɗe.
EFCC ta bayyana cewa ana zargin Sadiya Umar Farouq da amfani da muƙami ba daidai ba, haɗa baki da kuma karkatar da kuɗaɗen gwamnati.
Hukumar ta kuma buƙaci duk wanda ya san inda take da ya kai rahoto domin a kamo ta ta gurfana a gaban kotu.
Hukumar EFCC Na Neman Tsohuwar Minista Sadiya Umar Farouq Ruwa A Jallo

