Mutane 19 ne ake fargabar sun mutu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a a karamar hukumar Gwaram ta jihar Jigawa.
Shaidun gani da ido sun bayyana cewa hatsarin ya faru ne lokacin da tayar wata mota kirar Toyota Hummer ta fashe.Hakan yasa motar ta fadi ta kuma kama da wuta.
Mutanen da ake fargabar sun mutu sun fito ne daga karamar hukumar Katagum dake jihar Bauchi kuma suna kan hanyarsu ta zuwa garin Gadar Maiwa domin halartar biki.
Babu daya daga cikin fasinjojin dake motar da ya tsira da ransa.
Mai magana da yawun rundunar yansandan jihar Jigawa ya tabbatar da faruwar hatsarin sai dai bai bayyana yawan mutanen da abin ya rutsa da su ba.