Hatsarin mota ya sanadiyyar rasa rayukan mutane 19 a Jigawa

Mutane 19 ne ake fargabar sun mutu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a a karamar hukumar Gwaram ta jihar Jigawa.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa hatsarin ya faru ne lokacin da tayar wata mota kirar Toyota Hummer ta fashe.Hakan yasa motar ta fadi ta kuma kama da wuta.

Mutanen da ake fargabar sun mutu sun fito ne daga karamar hukumar Katagum dake jihar Bauchi kuma suna kan hanyarsu ta zuwa garin Gadar Maiwa domin halartar biki.

Babu daya daga cikin fasinjojin dake motar da ya tsira da ransa.

Mai magana da yawun rundunar yansandan jihar Jigawa ya tabbatar da faruwar hatsarin sai dai bai bayyana yawan mutanen da abin ya rutsa da su ba.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...