Gwamnoni ne matsalar Najeriya – Ghali Umar Na’Abba

Latsa hoton sama domin kallon bidiyon

Tsohon kakakin majalisar wakilai ta Najeriya Hon Ghali Umar Na’Abba ya zargi gwamnoni da cewa su ne matsalar Najeriya da ke kassara dimokaradiyya a ƙasar.

A hirarsa da BBC ya ce gwamnoni suka haddasa duk wani halin da yanzu Najeriya ta tsinci kanta a ciki.

Duk ana ganin dimokaradiyya a Najeriya wuyanta ya isa yanka, amma tsohon shugaban majalisar wakilan Najeriya na ganin da sauran aiki idan aka yi la’akari da manyan matsalolin da suka dabaibaye dimokuradiyyar Najeriya, a cewarsa saboda rashin dimokaradiyyar cikin jam’iyya da siyasar uban gida da kuma siyasar ɓangaranci.

Na’Abba wanda aka zaɓa ɗan majalisar tarayya a jam’iyyar PDP kafin ya koma APC, ya ce yanzu dukkanin manyan jam’iyyun babu wadda take bin tsarin dimokuradiyya.

“Yanzu ba ni da jam’iyya saboda ba dimokuradiyya ake ba, kuma ba a yin zaɓe.”

“Na janye daga takarar sanata saboda an bukaci dole sai na bayar da kudi a tsayar da ni,” in ji shi.

Ya shaida wa BBC cewa suna shirin kafa sabuwar jam’iyyarsu kuma zai nemi takarar kujerar sanata.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...