Gwamnatin tarayya na kashe miliyan ₦3.5 wajen ciyar da Elzakzaky a kowane wata

Ministan yada labarai, Alhaji Lai Muhammad ya ce gwamnatin tarayya tana kashe miliyan ₦3.5 a kowane wata wajen ciyar da Ibrahim Elzakzaky,shugaban kungiyar yan uwa musulmi ta Najeriya, da akafi sani da Shi’a.

Duk da belinsa da babbar kotun tarayya ta bayar, Elzakzaky ya gaza samun yanci tun lokacin da aka kama shi a shekarar 2015.

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ce ke cigaba da tsare shi a ofishin ta .

Gwamnatin tarayya ta sha nanata cewa tana cigaba da tsare Elzakzaky ne domin kare lafiyarsa saboda yana fuskantar barazana.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]