Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa gwamnatin jihar na kashe kimanin naira miliyan 150 duk wata domin samar da tsaftataccen ruwan sha ga al’umma.
Gwamnan ya bayyana hakan yayin da yake bayani kan matakan da gwamnatinsa ke ɗauka domin inganta samar da ruwa a birane da karkara.
A cewarsa, kuɗaɗen na tafiya ne wajen gyaran bututun ruwa da suka lalace, kula da na’urorin tace ruwa da sauran muhimman kayan aiki domin tabbatar da ci gaba da samar da ruwa mai tsafta.
Inuwa Yahaya ya ce gwamnati ta bai wa harkar ruwa muhimmanci saboda tasirinta wajen inganta lafiya da walwalar jama’a.
Ya kuma amince cewa har yanzu akwai ƙalubale sakamakon ƙaruwar jama’a da faɗaɗa birane da ƙauyuka, amma ya tabbatar da cewa gwamnati na ci gaba da faɗaɗa ayyukan ruwa a faɗin jihar.
Gwamnatin ta kuma buƙaci al’umma da su taimaka wajen kare kayayyakin ruwa tare da kai rahoton duk wata matsala ga hukumomin da suka dace.
Gwamnatin Gombe Na Kashe N150m Duk Wata Kan Samar Da Ruwa — a Cewar Gwamna Inuwa Yahaya

