Gwamnan Taraba Ya Kai Ziyarar Fadar Shugaban Ƙasa Inda Ya Shiga Ganawar Sirri Da Tinubu

Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya kai ziyara fadar shugaban ƙasa a Abuja, inda ya shiga wata ganawar sirri da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a safiyar Litinin.

Kefas ya isa Fadar Vila tare da Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, abin da ya nuna cewar wannan ita ce ganawarsa ta farko da Tinubu tun bayan komawarsa daga PDP zuwa APC.

A kwanakin baya an shirya masa taron tarbar shiga jam’iyyar APC a ranar 19 ga Nuwamba, amma ya dage bikin sakamakon harin sace ’yan makaranta mata a Maga, Jihar Kebbi, inda ya bayyana cewa bai dace a yi shagulgula a lokacin tashin hankali ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]