Ganduje ya ce ƙofar sulhu a buɗe take tsakaninsu da ɓangaren Shekarau


A cikin wata tattauanwa da BBC ta yi da shi, Ganduje, ya ce yanzu lokaci ne na tafiya tare da mayar da hankali kan harkokin ci gaban dimokraɗiyya.

Gwamnan na Kano, ya ce “Muna rokon ‘yan uwanmu a zo a hada a hannu gaba ki daya don a yi wannan tafiya tare, sannan kuma ina so na sanar da ‘yan jam’iyya cewa a dauka damara don yanzu za a shiga gwagwarmayar zabe”.

Ganduje ya ce “Yana da matukar muhimmanci shugabannin jam’iyya su san aikinsu ta yadda za a tafiyar da jam’iyya akan tafarkin dimokradiyya”.

Gwamnan ya ce, idan ana so a shirya ba a duba abubuwan da suka faru a baya, su fatansu azo a zama tsintsiya madaurinki daya.

Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya ce duk da batun za su daukaka kara zuwa kotun koli wannan daban domin dimokradiyya ce, kuma hakan ba zai hana azo a dai-daita a ci gaba da tafiya tare ba.

Ya ce.” Batun kwamitin da uwar jam’iyya ta nada ni shugabanci na yin sulhu yana nan yana jiransu domin duk mun yi tanadin yadda za a gudanar da dai-daitawar su kawai muke jira”.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]