Ebola ya kashe Bahagon ‘Yansanda a Marabar Nyanya

Abdurrazak Ebola ya yi nasarar doke Bahagon Shagon ‘Yansanda a damben mota da suka yi a marabar Nyanya ranar Lahadi.

Damben na gasar mota na jihar Kaduna ne, amma Umar Fiallo shugaban kungiyar damben Kaduna ya kai wasan Marabar Nyanya da ke jihar Nasarawa, Najeriya.

Tun da fara sai da aka bar matasa da manyan ‘yan dambe suka fafata a tsakaninsu kafin wasan Ebola da Bahagio.

Cikin wasannin da aka yi har da canjaras tsakanin Kurman Guramada da Bahagon Musan Kaduna daga Arewa.

Sai Garkuwan Bahagon Shagon ‘Yansanda daga Jamus ya doke Autan Dan Gero Guramada.

Sai da agogon ya kai sha biyu saura, sannan ne Umar Fiallo ya shiga fili ya zayyana dokokin damben tare da Idris Bambarewa shugaban damben jihar Nasarawa.

Daga nan ne Alkalin wasa Shagon Amadi ya daue hannun Ebola da Selotif da kuma na Bahagon ‘Yansanda.

Daga nan ne aka hura wasa suka fara dambe a tsakaninsu, inda suka yi minti uku turmin farko babu kisa aka raba.

Bayan da suka sha ruwa aka koma turmi na biyu ne Abdurrazak ya yi nasara a kan Bahagon Shagon ‘Yansanda.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...