Dubban masu zanga-zanga a Israi’la sun bukaci Firaministan kasar Benjamin Netanyahu ya sauka

Jama'a da dama a Israi'la na cikin wahala saboda matsalar tattalin arziki

Bayanan hoto,
Jama’a da dama a Israi’la na cikin wahala saboda matsalar tattalin arziki

Dubban ‘yan Israi’la sun gudanar da zanga-zanga a Tel Aviv, don nuna adawa da abinda suka kira kangin tattalin arziki da salon gwamnati na ‘yaki da annobar korona ‘ya tsunduma al’umma ciki.

Matasa da dama sun cika dandalin taro na Robin Square makil sanye da takunkumi, sai dai ba tare da bayar da tazara ba.

A birnin Kudus kuwa daruruwan mutane sun taru a kofar gidan Frai minista Benjamin Netanyahu, suna masu kiran ya sauka daga kan kujerarsa.

‘Yan sanda sun ‘yi amfani da barkonon tsohuwa da ruwan zafi, domin tarwatsa dubunnan masu zanga-zangar, abin da ‘ya rikide ‘ya koma tashin hankali.

Jama’ar na kuma nuna damuwa a kan yadda diyyar da gwamnati ke bayarwa ba ta isa garesu a kan lokaci.

Kananan yan kasuwa da ma’aikata masu zaman kansu da fitattun taurari ne suka shirya zanga-zangar, da ta samu tabarrakin jama’ar gari.

Mutane da dama a kasar sun tagayyara, kuma suna nuna takaici a kan yadda dokokin da aka kafa na ‘yaki da cutar ta korona a kasar ke cigaba da janyo musu wahala.

Bayanan hoto,
Masu zanga-zangar na cewa diyyar da gwamnati ke ba su ba ta isa wajensu a kan lokaci

Yayin da ma’aikatan gwamnati ke samun tallafi, su kuwa ma’aikata masu zaman kansu cewa suke har yanzu ba a cika musu alkawarin basu tallafin da aka musu ba.

Ranar Jumma’ar da ta gabata dai Frai ministan kasar Benyamin Netanyahu ‘ya gana da ‘yan gwagwarmaya domin tattauna matsalolinsu.

‘Ya shaida musu cewa gwamnatinsa, za ta ci gaba da kokarin biyan bukatun Jama’a, da suka hadar da biyansu alkawuran da aka musu na jin kai.

Tun a tsakiyar watan Maris ne hukumomi a Israila suka kakaba dokar kulle, domin ‘yaki da annobar korona.

Tun daga wancan lokaci zuwa yanzu, alkalumma sun nuna cewa an samu karuwar rashin aiki a kasar da kaso 21.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...