Dakarun STF Sun Hallaka Wasu Yan Bindiga A Filato

Dakarun dake aikin wanzar da zaman lafiya a jahar Filato sunyi nasarar hallaka wasu masu garkuwa da mutane su uku, suka kuma kwace makamai. 

Kakakin rundunar Tsaro ta Special Task Force a Jahar Filato, Manjo Ishaku Takwa ya ce tun a baya, jami’an tsaro na bibiyan gungun masu garkuwa da mutanen, wanda suke da tabbacin suna cikin wadanda suka fasa gidan yarin Jos, a watan Nuwamban bara.

A cikin kwanakin nan, jami’an tsaron na STF sun yi nasarar kwato mutane da aka yi garkuwa da su, ba tare da sun sami lahani ba.

Gwamnan jahar Filato, Simon Lalong wanda ya yaba wa jami’an tsaron bisa kokarin nasu, ya kuma yi alkawarin sanya hannu don kisan duk wanda kotu ta tabbatar ya aikata laifin yin garkuwa da mutane don neman kudin fansa.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...