Buhari ya rattaba hannu kan dokar albashi mafi karancin

Shugaba Buhari

Hakkin mallakar hoto
Twitter/@BashirAhmad

Shugaba Najeriya, Muhammadu Buhari, ya sa hannu kan dokar karin albashi mafi karanci na naira 30,000 a fadin tarayyar Najeriya.

Hakan yana nufin daga wannan watan N30,000 shi ne albashi mafi karanci da ma’aikata za su karba a fadin Najeriya baki daya, kamar yadda fadar shugaban ta bayyana a shafinta na Twitter ranar Alhamis.

“Shugaba Buhari ya sanya wa sabuwar dokar mafi karancin albashi hannu. Daga yanzu N30,000 ne mafi karancin albashin,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa “dokar za ta fara aiki nan take kuma ta shafi kowane ma’aikaci.”

A ranar Litinin ne kungiyar kwadago ta NLC ta bai wa Shugaba Buhari zuwa 1 ga watan Mayu a matsayin wa’adin ko dai ya saka hannu a kan dokar, ko kuma ta dauki mataki.

Tun a shekarar 2015 ne Buhari ya yi alkawarin yi wa dokar kwaskwarima.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...