Boko Haram: Sojoji sun ce sun kama ‘yan Boko Haram 10 a Kano

Boko Haram sun soma kaddamar da hare-hare a 2009

Asalin hoton, Boko Haram

Bayanan hoto,
Boko Haram sun soma kaddamar da hare-hare a 2009

Rundunar sojojin Najeriya ta yi ikirarin kama mutanen da take zargi da kasancewa ‘yan kungiyar Boko Haram a birnin Kano da ke arewa maso yammacin kasar.

Mai magana da yawun rundunar, Njoko Irabor, wanda ya tabbatar wa BBC hakan, ya ce sun kama mutanen ne a wani masallaci da ke unguwar Hotoro a cikin birnin Kano ranar Asabar.

Ya ce sun kamo mutanen ne a wani samame da suka kai masallacin bayan samun bayanan sirri a kansu.

A cewarsa, suna ci gaba da faÉ—aÉ—a binciken da tattara bayanan sirri da zummar inganta tsaro a jihar ta Kano.

Rahotanni sun ce wannan kamen ya tayar da hankulan mazauna wasu yankunan birnin na Kano.

Wannan ne karon farko cikin lokaci mai tsawo da hukumomi suke sanar da kama wadanda ake zargi da kasancewa ‘ya’yan kungiyar ta Boko Haram a jihar Kano.

A shekarun baya, birnin na Kano ya yi fama da hare-hare na mayakan kungiyar, wadanda suka taba tashin bam a babban masallacin da ke kofar gidan Sarkin Kano da kuma wasu wurare.

Rundunar sojin ta kama mutanen ne a yayin da kungiyar Boko Haram ke matsa kai hare-hare musamman a Arewa maso gabashin kasar.

Bayanan bidiyo,
Abdussalami Abubakar: Tsohon shugaban Najeriya ya koka kan matsalar tsaro

A watan jiya mayakan kungiyar sun hari garin Geidam da ke jihar Yobe inda suka kashe mutanen da dama sannan suka tilasta wa daruruwan mutane tserewa daga gidajensu zuwa wasu garuruwa.

Kazalika mayakan kungiyar ta Boko Haram sun kafa tuta a wasu kananan hukumomi biyu na jihar Neja da ke arewa maso tsakiyar Najeriya, kamar yadda gwamnan jihar Sani Bello, ya shaida wa manema labarai a watan jiya.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ÆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...