BBC Hausa: United ta koma ta biyu a Premier kan wasan Man City

Marcus Rashford

Asalin hoton, Getty Images

Manchester United ta koma ta biyu a Premier League, bayan cin Leeds United 2-0 a wasan mako na 23 ranar Lahadi.

Marcus Rashford ya fara cin kwallo a minti na 80, kuma na 13 da ya zura a raga tun bayan kammala gasar kofin duniya.

Ba dan wasan da ya kai Rashford yawan zura kwallaye a raga tun bayan da aka kammala gasar kofin duniya a Qatar a 2022.

Sauran minti biyar a tashi daga wasan a Elland Road, United ta kara na biyu ta hannun Alejandro Garnacho, wanda hakan ya sa ta hada maki uku.

United ta ci kwallo biyu amma ba a karba ba, har da wadda Rashford ya kara a raga.

Da wannan sakamakon United ta koma mataki na biyu a teburin Premier League da maki 46.

Manchester City za ta karbi bakuncin Aston Villa a Etihad a wasan mako na 23 a babbar gasar tamaula ta Ingila ranar Lahadi.

City, mai rike da Premier na bara tana ta uku da maki 45 a teburin bana.

Golan Manchester United, David de Gea ya yi wasa na 400 a Premier League, shine na farko da ba dan Birtaniya ba da ya yi wannan bajintar.

Ranar Laraba United da Leeds suka tashi 2-2 a kwantan wasan Premier League mako na takwas a Old Trafford.

United ta ci wasa na shida a waje a bana kenan, wadda a bara ma fafatawa shida ta yi nasara a karawar da ta kai ziyara a bara.

Kuma a wasa biyar da ci a bana a waje, duk da 1-0 ta yi nasara.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...