Bankin Duniya Ya Hango Bunƙasar Tattalin Arzikin Najeriya A 2026 Da 2027

Bankin Duniya ya ce tattalin arzikin Najeriya na kan hanyar samun bunƙasa mafi girma cikin fiye da shekara goma da suka gabata.

A cewar bankin, ana sa ran tattalin arzikin ƙasar zai ƙaru da kashi 4.4 cikin 100 a shekarun 2026 da 2027.

An bayyana wannan hasashe ne a sabon rahoton ci gaban tattalin arzikin duniya, Global Economic Prospects, da Bankin Duniya ya fitar a ranar Talata.

Sai dai wasu masana sun ce hasashen bai yi la’akari da halin rayuwa da kuma ƙalubalen da al’ummar ƙasar ke fuskanta a halin yanzu ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]