Ban damu da wanda zai gaje ni ba a 2023 – Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa bai damu da wanda zai gaje shi ba a matsayin shugaban Æ™asa saboda “ya ajiye rahoton komai da komai”.

Shugaban ya faÉ—i hakan ne a hirarsa da kafar talabijin ta Channels TV a yammacin Laraba, yana mai cewa “zaÉ“en 2023 ba matsalata ba ce”.

“Ban damu da wanda zai gaje ni ba, rabu da shi ya zo ko ma wane ne,” in ji shi.

Da yake amsa tambaya kan ko me ke zuwa masa a rai idan ya ji an ambaci zaÉ“en 2023, Buhari ya amsa da cewa: “Ba matsalata ba ce.”

Da aka tambaye shi: “Ba ka damu game da wanda zai gaje ka ba? Sai ya ce:

“Bar shi ya zo ko ma wane ne. Na tabbata na ajiye rahoton duk wani abu mai muhimmanci. Bai kamata wani ya kira ni ba da shaida a gaban kotu ba a kan wani abu, idan ba haka ba kuma zai shiga matsala.”

Buhari ya ce duk da cewa ba shi da wani É—an takara da yake goyon baya a jam’iyyarsu ta APC mai mulki ya gaje shi amma idan ya bayyana shi za a iya halaka shi.

“A’a, saboda idan na faÉ—a za a iya kawar da shi. Gara na bar shi a sirrance,” a cewarsa.

‘Mun ayyana ‘yan fashin daji ‘yan ta’adda saboda abin da suka sani kenan’

Buhari ya amsa tambayoyi kan batutuwa da dama yayin hirar da aka naÉ—a a fadarsa ta Aso Rock Villa, ciki har da matsalar ‘yan fashin daji na arewa maso yamma.

“Mun ayyana su a matsayin ‘yan ta’adda…saboda shi ne kaÉ—ai abin da za su fahimta,” a cewarsa.

Sai dai babu wata sanarwa da ta nuna cewa gwamnatin ta ayyana su ‘yan ta’adda a hukumance tun bayan da Ministan Shari’a Abubakar Malami ya nemi kotu ta ba su damar yin hakan duk da cewa kotun ta amince da buÆ™atar gwamnatin.

‘Ba za mu saki Nnamdi Kanu ba’

‘Yan makonni bayan alÆ™awarin da ya yi wa dattawan al’ummar Ibo na duba yiwuwar sakin É—an tawaye Nnamdi Kanu, Buhari ya ce “ba za mu iya sakin sa ba”.

Ya ce: “Akwai sashen da ba zan iya taÉ“awa ba, shi ne na shari’a. Batun Kanu yana gaban kotu. Amma abin mamakin shi ne, lokacin da yake Turai yana zagin wannan gwamnati, na zaci zai so ya zo ya kare kansa daga waÉ—an nan zagr-zargen.

“Saboda haka muna ba shi dama ce ta kare kan sa bisa tsarinmu, ba wai ya koma Turai ya ci gaba da zaginmu ba kamar ba É—an Najeriya ba. Ya zo nan ya soke mu…waÉ—anda ke cewa ya kamata a sake shi, a’a, ba zamu iya sakin sa ba.”

A watan Nuwamba ne dattawan suka gana da Buhari a Abuja, inda suka nemi ya tausaya wa jagoran na haramtacciyar ƙungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB) da ke neman kafa ƙasar Biafra a kudu maso gabashin Najeriya.

Ba na goyon bayan zaÉ“en ‘yar tinÆ™e – Buhari

Shugaban ya ce ba ya goyon bayan tsarin zaÉ“e na ‘yar tinÆ™e yayin zaÉ“en ‘yan takara a cikin jam’iyyun siyasa, wanda sabuwar dokar zaÉ“e ta tanada.

Buhari ya ce ya kamata a bai wa ‘yan Najeriya zaÉ“i uku, ba wai ‘yar tinke kawai ba.

“Abin da nake cewa shi ne, ba zai yiwu ka taÆ™aita zaÉ“in al’umma ba a kan abu É—aya kawai kuma ka ce dimokuraÉ—iyya kake yi. Dole ne a ba su ‘yancin zaÉ“i uku,” in ji shi.

A cewarsa: “Akwai ‘yar tinÆ™e da jefa Æ™uri’a da kuma masalaha.”

Bai kamata a Æ™irÆ™iri ‘yan sandan jihohi ba – Buhari

Shugaba Buhari ya ce “babu maganar Æ™irÆ™irar ‘yan sandan jihohi” yayin da yake maganar rikicin makiyaya da manoma.

Shugaban ya kamanta Æ™irÆ™irar ‘yan sandan jihohi da kuma alaÆ™a tsakanin Æ™ananan hukumomi da gwamnatin jihohinsu.

Ya ce: “Ko a yanzu kun ga gwamnatocin jiha na bai wa Æ™ananan hukumomi haƙƙinsu?”

More News

Gwamnatin jihar Kaduna ta kafa kwamitin biyan diyya ga mutanen da harin jirgin sama ya shafa

Gwamnatin jihar Kaduna, ta kafa wani kwamiti da zai biya diyya tare da tallafi ga mutanen da harin jirgin sama marar matuki na rundunar...

Uba Sani ya bayar da umarnin yin bincike kan harin soja da ya kashe mutane 30

Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba sani ya bayar da umarnin bincike kan harin jirgin sama da ya kashe mutane da dama a ƙauyen...

APC ta lashe zaɓen dukkanin shugabannin ƙananan hukumomin jihar Ekiti

Jam'iyar APC ta lashe dukkanin zaɓen shugabannin kananan hukumomin jihar Ekiti da kuma na kujerun kansiloli 177 da aka gudanar. A ranar Asabar ne...

APC ta lashe zaɓen dukkanin shugabannin ƙananan hukumomin jihar Ekiti

Jam'iyar APC ta lashe dukkanin zaɓen shugabannin kananan hukumomin jihar Ekiti da kuma na kujerun kansiloli 177 da aka gudanar. A ranar Asabar ne...