Babu sunan Tambuwal a cikin ‘yan takarar gwamnan Sokoto

Aminu Waziri Tambuwal


Aminu Waziri Tambuwal ne ya zo na biyu a zaben fitar da gwani na PDP

Hukumar zaben Najeriya reshen jihar Sokoto ta ce babu sunan gwamnan jihar Aminu Waziri Tambuwal a jerin sunayen wadanda suka cancanci tsayawa a zaben 2019.

Kwamishinan hukumar zaben jihar, Malam Sadik Abubakar Musa, ya shaida wa BBC cewa jam’iyyar PDP mai hamayya, ta mika sunan Alhaji Mannir Dan Iya ne a matsayin dan takararta na mukamin gwamnan.

Wannan dai ya saba wa tunanin mutane da dama a jihar cewa Alhaji Aminu Waziri Tambuwal ne jam’iyyarsa ta PDP za ta tsayar takarar gwamna bayan da ya kasa samun tikitin takarar shugabancin kasar a watan Satumba.

  • Tambuwal zai tsaya takarar shugaban kasa
  • Abin da ya sa na koma PDP – Tambuwal

Da ma dai Alhaji Dan Iyan ne ya samu tikitin takarar gwamnan babu hamayya a zaben fitar da gwani na ranar a watan Satumba, amma sai wasu majiyoyin jam’iyyar suka ce ya amince ya janye wa gwamnan jihar bayan da ya fadi a zaben fitar da gwani na shugaban kasa.

Sai dai jami’in hukumar zaben ya ce jam’iyyar na da har nan da ranar daya ga watan Disamba ta sauya sunan dan takarar idan tana bukatar yin hakan.

“Jam’iyyun suna da lokaci wanda za su iya canza sunan ‘yan takara ko kuma dan takara ya ce ya janye. Daga nan har ranar 1 ga watan Disamba za su iya yin hakan,” in ji shi.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]