Atiku ya sanya hannu a yarjejeniyar zaman lafiya

Tsohon shugaban Najeriya Abdussalam Abubakar tare da Atiku Abubakar da shugaban jam'iyyar PDP Uche Secondus

Tsohon shugaban Najeriya Abdussalam Abubakar tare da Atiku Abubakar da shugaban jam’iyyar PDP Uche Secondus

Dan takarar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya ya sanya hannu a kan takardar yarjejeniyar zaman lafiya gabanin zabukan da za gudanar a shekara mai zuwa.

Shugaban jam’iyyar ta PDP Uche Secondus ne ya bayyana haka a shafinsa na Tiwita.

Mista Secondus ya bayyana cewa ya jagoranci Atiku Abubakar zuwa cibiyar Bishop Kukah da ke Abuja inda ya sanya hannu a kan yarjejeniyar.

    A jiya ne dai ‘yan takarar mukamin shugaban kasa a Najeriya suka rattaba hannu a kan takardar yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya.

    Cikin wadanda suka halarci taron akwai Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.

    Amma Atiku Abubkar bai halarci taron ba duk da cewa tsohon shugaban Najeriya Abdussalam Abubakar wanda shi ne ke jagorantar wannan kokarin ya ce kwamitinsa ya gayyaci dukkan jam’iyyun siyasar kasar zuwa wajen wannan taron.

    More from this stream

    Recomended

    Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

    Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]