Dan wasan baya na Chelsea, David Luiz, na daya daga cikin ‘yan kwallon da Arsenal ke nema domin karfafa bangaren baya na kungiyar.
Luiz, wanda kwantiraginsa zai kare a shekarar 2021, bai yi atisayi da tawagar manyan ‘yan kwallon kungiyar ba a ranar Laraba.
Dan wasan mai shekara 32 ya halarci atisayen a Cobham kuma bai bijirewa wani umarni ba – amma dai ba a yi komai da shi ba.
Arsenal za ta fara kakar Firimiya ta bana a Newcastle ranar Lahadi, yayin da Chelsea za ta ziyarci Manchester United.