An samu gobara a matatar mai ta  Dangote

Gobara ta ƙone wani sashe na matatar man fetur ta Dangote.

Lamarin ya faru ne a ranar  Larabar.

Da yake magana da manema labarai, Anthony Chijiena mai magana da yawun rukunin kamfanonin Dangote ya ce gobarar ta kama ne a sashen da ake tace gurbataccen ruwa dake matatar.

Ya ce tuni aka shawo kan wutar ya ƙara da cewa gobarar bata yi muni sosai ba.

Ya ƙara da cewa babu damuwa sosai domin matatar na cigaba da aiki kamar yadda aka saba.

A ranar 12 ga watan Yuni ne matatar ta Dangote ta fara aiki ka’in dana in inda aka fara ta ce man Diesel da kuma na jirgin sama.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]