
Gwamnatin jihar Cross River ta sanar da cewa an samu wani mutum guda dake dauke da cutar Covid-19 a jihar.
A cewar kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Henry Ayuk ne ya bayyana haka a wurin taron manema labarai da ya gudanar a ranar Talata.
Ya ce wanda aka samu dauke da cutar wani ɗan ƙasar China ne mai shekaru 53 dake aiki a kamfanin siminti na Lafarge dake ƙaramar hukumar Akamkpa kuma ya shigo Najeriya ne a ranar 17 ga watan Maris kuma babu jimawa alamun cutar suka bayyana tare da shi.
A cewar kwamishinan halin da marar lafiyan yake ciki ya tsananta a asibitin gwamnatin jihar abun da ya sa aka yi gaggawar mayar da shi Asibitin Koyarwa na Jami’ar Calabar inda aka yi masa gwaji kuma aka tabbatar yana ɗauke da cutar.
Ayuk ya kara da cewa an sake karfafa ma’aikatar lafiya ta jihar domin ya shawo kan annobar inda ya kara da cewa kada al’umma su tayar da hankulansu.
“Amma yanzu muna farin cikin sanar da cewa yana samun samun sauki, ” a cewar kwamishinan.

