An Rufe Hanyar Abuja Zuwa Kaduna

Hukumar da ke kula sufurin jiragen kasa na Najeriya NRC ta dakatar da jigilar da jiragenta ke yi akan hanyar Abuja zuwa Kaduna.

Daukan wannan mataki ya biyo bayan rahotanni da suka nuna cewa an kai hari kan hanyar layin dogon da ta ratsa yankin Rijana da Duste a jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin kasar.

Jaridun Najeriya sun ruwaito cewa Babban Darektan hukumar ta NRC Fidet Okhiria ya tabbatar da dakatar da jigilar sannan ya ce ana kan gudanar da bincike.

Hukumar ta NRC ta dora alhakin harin akan masu barnata dukiyar gwamnati yayin da wasu ke cewa ‘yan fashin daji ne.

Bayanai sun yi nuni da cewa harin wanda aka dasa abin fashewa akan hanyar jirgin, ya yi sanadin karyewar turakun jirgin ta yadda ba zai iya wucewa ba.

Gabanin hakan tsohon Sanata a jihar ta Kaduna, Shehu Sani ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa an kai hari akan jirgin kasa da ke zirga-zirga tsakanin Abuja zuwa Kaduna.

Wasu hotunan da suka karade shafukan sada zumunta sun nuna yadda fashewar ta karya hanyar jirgin da kuma yadda aka kai hari kan sashen direban jirgin.

Wannan lamari ya sa ala tilas aka mayar da fasinjojin da suka taso daga Abuja zuwa inda suka fito bayan aukuwar wannan lamari.

Matsalar masu garkuwa da mutane da ke tare hanyar mota ta sa jama’a da dama sun koma tafiya ta jirgin kasa don gujewa fadawa tarkon masu satar mutanen.

Wannan dai ba shi ne karon farko da ake kai harin kan jiragen kasa da ke zirga-zirga tsakanin Abuja da Kaduna ba.

(DailyPost)

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...