An kama wata yar kunar bakin wake a Maiduguri

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta kama wata mata yar kunar bakin wake wacce ta yi yunkurin shiga birnin Maiduguri.

A wani sako da rundunar ta wallafa a shafinta na Twitter rundunar ta ce dakarunta na bataliya ta 251 sun tare yar kunar bakin wake a Gonikalachari.

“Sojojin Bataliya ta 251 dake Maiduguri sun kama wata mace yar kunar bakin wake wacce tayi kokarin shiga birnin Maiduguri ta tayar da bom din dake jikinta domin tayi barna kan yan Najeriya da basu ba su gani ba,” sakon ya ce.

Da aka yi mata tambayoyi yar kunar bakin waken mai shekaru 19 ta ce sunanta Shaidatu kuma ta fito ne daga Gwoza.

Kuma an turo ta ne ita kaɗai ta kai harin bayan da ta shafe shekaru 3 a Dajin Sambisa.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]