An Kama Mata 3 Da Ake Zargin Sun Yi Hadin Baki Da ISWAP a Sansanin ’Yan Gudun Hijira Na Borno



Sojojin Najeriya sun kama wasu mata uku da ake zargin suna hada kai da kungiyar ISWAP a karamar hukumar Konduga da ke jihar Borno.

Masanin harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi, Zagazola Makama, ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafin X.

Rahotanni sun ce an gudanar da samamen ne bayan samun bayanan sirri da kuma cafke wasu sakonnin sadarwa da suka nuna yunkurin kai wata mata zuwa yankin da ’yan ta’adda ke iko da shi.

Dakarun Bataliya ta 222 sun kama matan ne a wani sansanin ’yan gudun hijira da ke Konduga.

Makama ya ce ana zargin matan da taimaka wa ’yan ta’adda wajen sadarwa da zirga-zirga tsakanin fararen hula da kungiyoyin ta’addanci.

Ya kara da cewa jami’an soji sun tsare wadanda ake zargin domin ci gaba da bincike.

More from this stream

Recomended