Fadar masarautar Katsina ta fitar da wata sanarwar a jiya, wadda a ciki ta aike sakon jaje ga daukacin jama’arta kan ibtila’in kashe-kashen da mutanen gundumomin Batsari, da Dan-Musa, da Kankara sa Wagini da sauransu wuraren da abun ya shafa suka samu kansu a ciki.
Sakataren masarautar Alhaji Bello M IFO shi ne ya fitar da ita, tare da shaidawa jama’a ce wa sakamakon halin da suka samu kansu a ciki na alhiji da jimami masarautar ta yanke shawarar a wannan karon ba za a yi hawan sallah kamar yadda aka saba ba.
Alhaji Bello ya ce Mai-martab sarkin Katsina Dr Alhaji Abdulmumin Kabir Usman CFR da majalisar masarautar ne suka ga dacewar dage duk wasu shagulgula dan nuna alhini kan abin da ya samu jama’arsu.
A karshen sanarwar ta ce za a je sallar Idi kamar yadda aka saba, da yin addu’o’in neman zaman lafiya ga jihar Katsina da Najeriya baki daya.