An Bukaci Fulani Su Saka ‘Ya ‘Yansu a Makaranta Don Yakar Jahilci

Shugaban kungiyar, reshen jahar Nasarawa, Alhaji Bala Mohammad Dabo ya ce sun tattauna ne kan hanyoyin magance matsalolin rashin zaman lafiya tsakaninsu da manoma.

Ya kara da cewa sun ja hankalin al’ummar Fulani da su sanya ‘ya’yansu a makarantu don yakar jahilci dake sanya su shiga wadansu halaye da ba su dace ba.

Yahaya Musa Jibrin dake aikin wanzar da zaman lafiya a yankin Gindin Akwati dake karamar hukumar Barkin Ladi a jahar Filato, ya ce kungiyarsu tare da hadin gwiwan jami’an tsaro, na zakulo masu aikata laifi.

Dangantaka tsakanin makiyaya da manoma a jahar Filato ta fara armashi bayan da wani manomi mai suna Solomon a kauyen Bisichi dake karamar hukumar Barkin Ladi, ya yafe barnar da dabbobin wani makiyayi, Ibrahim suka yi masa a gonarsa.

(VOAHausa)

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...