Amnesty Int′l ta zargi jami′an tsaron Najeriya | Labarai

Kungiyar Amnesty Int’l, ta zargi jami’an tsaron Najeriya da amfani da karfi fiye da kima a kan fararen hula masu neman ballewa a yankin kudu maso gabashin kasar.
Kungiyar ta Amnesty ta kuma yi zargin jami’an sun kashe akalla mutane 115.
Sai dai rikicin da ya taso jihohin ‘yan kabilar Igbo a bana, ya yi sanadin salwantar jami’an ‘yan sanda 127 a cewar ‘yan sandan.
Akwai ma wasu ofisoshin ‘yan sanda 20 da na hukumar zabe da aka lalata, kamar yadda kafofin watsa labaran cikin Najeriyar suka tabbatar.
An dai zargi kungiyar IPOB mai rajin kafa kasar Biafra ta Igbo zalla da kuma wata Eastern Security Network, ESN, a takaice da aikata aika-aikar. Amma kungiyar IPOB ta Nnamdi Kanu, ta musanta zarge-zargen.
Amnesty Int’l dai ta dora alhakin kashe-kashen fararen hulan ne a kan ‘yan sanda da kuma jami’an DSS.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...