
Hukumar Aikin Hajji ta Kasa NAHCON ta tabbatar da cewa alhazan Najeriya da basu gaza 54 ne aka kwantar asibiti a kasar Saudiyya a yayin da aka tabbatar da mutuwar wasu alhazan huɗu a lokacin da ake cigaba da gudanar da aikin hajjin shekarar 2026.
Shugaban tawagar likitocin dake kula da alhazan ne ya bayyana haka a lokacin da yake yan jaridu jawabi kan walwala da kuma lafiyar alhazan a Makkah.
A cewarsa yanzu haka hukumar NAHCON tana gudanar da asibitoci guda biyar dake da lasisi da suka haɗa da biyu a Madina uku a Makkah domin kula da lafiyar alhazan Najeriya a matakin farko.
Asibitocin dake Madinah suna otal ɗin Alsham’s Markazia da kuma Buna Toiba dukkansu a unguwar Markazia a yayin da na Makkah suke a Misfalah, Sharasittin da Niger House da kuma Yabalash.

