Akwa Ibom: An kama masu fasa kaurin shinkafa daga kasar Kamaru

Dakarun Sojan Ruwan Najeriya a jihar Akwa Ibom sun kama wasu mutane shida tare da kwace buhuna 416 na shinkafar da aka haramta shigowa da ita daga hannun mutanen.

Da yake magana a Ibaka a wurin mika mutanen da ake zargi tare da shinkafar ga hukumar kwastam ta Najeriya kwamandan sansanin rundunar sojan ruwan dake Ibaka a karamar hukumar Ibaka Mbo, Kaftin Toritseju Vincent ya ce rundunar sojan ruwan za ta cigaba da iya bakin kokarinta wajen kawo ƙarshen fasa kwaurin shinkafa.

Kwamandan shiya na hukumar ta kwastam,Kolade Iloyede shine ya karbi mutanen da ake zargi tare da shinkafar daga sojan ruwan inda ya yi alkawarin gurfanar da su gaban shari’a su fuskanci hukunci domin haka ya zama izina ga masu aikata haka.

Daya daga cikin mutanen da ake zargi,Abia Etim ya musalta cewa yana da hannu a fasa kaurin inda ya ce shi fasinja ne kawai a cikin jirgin da aka kama bayan da ya hawo jirgin daga kamaru zuwa Najeriya.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...