Abin da zai sa Barca ta lashe La Liga ranar Asabar|BBC Hausa

La Liga

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

A ranar Asabar za a ci gaba da buga gasar La Liga wasan mako na 35, inda Barcelona za ta karbi bakuncin Levante.

A wasan farko da suka kara a gasar ranar 16 ga watan Disambar 2018, Barcelona ce ta yi nasara da ci 5-0.

Wadanda suka ci wa Barca kwallayen sun hada da Luis Suarez da Gerard Pique da kuma Lionel Messi wanda ya ci uku rigis a karawar.

Tun a ranar Laraba aka sa ran kungiyar ta Camp Nou za ta daga kofin La Liga, bayan da ta doke Alaves 2-0, sai dai kuma Atletico Madrid da ta ci Valencia 3-2 ya sa sai ranar Asabar za a mallaka mata kofin.

A wasan da Barcelona za ta karbi bakuncin Levante shi ne zai sa ta lashe kofin La Liga na bana da zarar daya daga abu uku ya faru ranar Asabar.

  1. Idan Atletico ta yi rashin nasara a karawa da Real Valladolid, za a bai wa Barcelona kofi tun kan ta fafata da Levante, da yake Atletico ce za ta fara yin wasa.
  2. Idan Atletico ta yi canjaras da Valladolid a ranar Asabar, ita ma Barca na bukatar canjaras ta lashe kofin La Liga na shekarar nan.
  3. Idan kuma Atletico ta ci wasanta ranar Asabar, ita ma Barcelona na bukatar doke Levante da zai sa a mika mata kofin La Liga na 26 jumulla.

Lionel Messi na Barcelona shi ne kan gaba da ya ci kwallo 33 a gasar La Liga, sai Karim Benzema na Real Madrid da Luis Suarez na Barcelona da kowanne keda 21 a raga.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Wasannin mako na 35 ranar Asabar 27 ga watan Afirilu.

  • Athletic de Bilbao da Deportivo Alaves
  • Atletico de Madrid da Real Valladolid
  • Leganes da Celta de Vigo
  • Barcelona da Levante

Karawar ranar Lahadi 28 ga watan Afirilu

  • Valencia da SD Eibar
  • Girona da Sevilla
  • Real Sociedad da Getafe
  • Villarreal da Huesca
  • Rayo Vallecano da Real Madrid

Fafatawar Litinin 29 ga watan Afirilu

Barcelona tana mataki na daya a kan teburi da maki 80, sai Atletico Madrid ta biyu mai maki 71, yayin da Real Madrid ta hada maki 64, ita ce ta uku a teburin na La Liga.

Kungiyar ta Nou Camp na fatan lashe kofi uku a bana, inda za ta fafata da Liverpool a wasan daf da karshe a Champions League, sannan ta kai karawar karshe a Copa del Rey.

Hakkin mallakar hoto
BBC Sport

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...