Abacha ya yaudari ‘yan siyasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin sojin Najeriya Sani Abacha, wanda ya mulki kasar daga 1993 har lokacin mutuwarsa a 1998, ya hau mulkin ne bayan ya yaudari ‘yan siyasa, a cewar Janar Ibrahim Badamasi Babangida.

Janar Babangida ya bayyana haka ne a hirarsa da Trust TV

, yayin da yake bayyana yadda Abacha ya yi yaudari mutane ya kwace mulki.

Abacha, wanda IBB ya bayyana a matsayin “babban abokina”, ya kasance hafsan hafsoshin sojoji a lokacin mulkin Babangida daga 1985, kuma daga baya ya nada shi Ministan Tsaro a 1990.

Babangida ya ce, gwamnatin Abacha tana da wayo. Sun san wadanda suka fi magana a kan zabe da juyin mulkin da batun 12 ga watan Yuni da sauran abubuwa.

Sai suka fara magana da su, suka yaudare su da karfafa musu guiwa su kawar da gwamnatin rikon-kwarya, da cewar idan sun kawar da gwamnatin rikon-kwaryar, za su dawo da su, su ba su abin da suke so mulkin dumokuradiyya, daga nan sai a kafa gwamnatin farar hula.

Babangida ya ce: ”Da wannan suka yaudari jama’a da sauran fitattun mutane, saboda haka da Abacha ya shigo, sai ake ta murna, hankali ya kwanta; Madalla abu ya yi kyau! Abin da zai faru a gaba kuma shi ne zababbiyar gwamnatin dumokuradiyya. Ni na sani, mun sani, hakan ba zai yiwu ba saboda maganar ita ce: (Abacha zai ce ), Me zai sa in sa kaina cikin hadari, kawai in zo in danka muku mulki?’ Wannan shi ne abin da ya faru.” In ji Babangida.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]