Jam’iyyar APC a jihar Kebbi ta karɓi fiye da mutum 10,000 da suka sauya sheƙa daga jam’iyyun ADC da PDP, ciki har da shugabannin jam’iyya na wasu ƙananan hukumomi da wasu fitattun masu ruwa da tsaki a siyasa.
Gwamna Nasir Idris ya tarbi sabbin mambobin a Fadar Gwamnatin jihar da ke Birnin Kebbi, inda ya tabbatar musu da cewa za su samu cikakkiyar dama da adalci a cikin jam’iyyar. Ya kuma buƙaci shugabannin APC a faɗin jihar su rungumi sabbin mambobin tare da haɗa su cikin harkokin jam’iyyar.
Da yake magana a madadin magoya bayan Sanata Garba Musa Maidoki na ADC, Bello Doya ya ce sun sauya sheƙa ne domin mara wa ayyukan ci gaban gwamnatin Idris baya.
Haka kuma, shugaban ƙungiyar shugabannin PDP na ƙananan hukumomi a jihar da wasu jami’an jam’iyyar sun koma APC. Shugaban Ƙaramar Hukumar Bunza, Bello Manti, ya ce kyakkyawan salon shugabancin Gwamna Idris ne ya ƙarfafa musu gwiwar sauya sheƙa.
Fiye Da Mutum 10,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa APC A Kebbi

