Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun kuɓutar da mutum huɗu da aka yi garkuwa da su bayan sun daƙile harin da wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne suka kai a yankin Surimi da ke ƙaramar hukumar Danko-Wasagu a Jihar Kebbi, kusa da iyakar Jihar Sakkwato.
Rundunar Sojin Najeriya ta bayyana cewa sojojin sun kai ɗauki ne bayan samun sahihan bayanan sirri kan ayyukan masu garkuwa da mutane a yankin.
A cewar rundunar, da suka fuskanci ƙarfin wutar sojoji, maharan sun tsere cikin daji tare da barin mutanen da suka sace, waɗanda daga bisani aka haɗa su da iyalansu.
Sojojin sun kuma tabbatar da cewa babu wani jami’insu da ya jikkata a yayin wannan samame.
Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutum Huɗu Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi

