NiDCOM Ta Karrama Farfesa Hakeem Tijani Da Lambar Yabon ‘Yan Najeriya Mazauna Ƙasashen Waje



Hukumar ‘Yan Najeriya Mazauna Ƙasashen Waje (NiDCOM) ta zaɓi Farfesa Hakeem Ibikunle Tijani, wani malamin jami’a ɗan Najeriya da ke zaune a Amurka, domin ba shi lambar yabo ta National Diaspora Merit Award (NDMA) 2026.

Hukumar ta ce an zaɓe shi ne saboda irin gudummawar da yake bayarwa wajen bunƙasa fannin ilimi da kuma ci gaban Najeriya.

NiDCOM ta bayyana cewa ana gudanar da bikin Ranar ‘Yan Najeriya Mazauna Ƙasashen Waje duk shekara domin girmama gudummawar ‘yan Najeriya da ke zaune a ƙasashen waje.

Za a gudanar da bikin ranar Diaspora a 24 ga Yuli, sannan a gabatar da lambar yabon NDMA a ranar 25 ga Yuli, 2026, a Banquet Hall da ke Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja. Hukumar ta kuma buƙaci masu son halartar taron su yi rajista ta shafinta na intanet.

More from this stream

Recomended