Gwamnatin Tarayya ta dawo da karin ‘yan Najeriya 39 daga birnin Johannesburg na ƙasar Afirka ta Kudu zuwa Legas, a wani shirin kwashe ‘yan ƙasar da jirgin Air Peace ya gudanar.
An bayyana cewa an shirya wannan jigilar ne domin mutanen da ba su samu damar hawa jirgin farko ba, a ci gaba da ƙoƙarin dawo da ‘yan Najeriya da rikicin nuna ƙyamar baƙi ya shafa a Afirka ta Kudu.
Gwamnatin ta yabawa kamfanin Air Peace saboda goyon bayan da ya bayar wajen gudanar da aikin.
Haka kuma ta sanar da cewa ana sa ran jigila ta ƙarshe za ta gudana a mako mai zuwa, inda za a dawo da kusan ‘yan Najeriya 300 zuwa ƙasar. Ta kuma jaddada cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta ci gaba da kare muradun ‘yan Najeriya tare da tabbatar da dawowarsu cikin aminci.
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karin ‘Yan Najeriya 39 Daga Afirka Ta Kudu

