Tinubu zai sake  tsayawa takara tare da Shettima a zaɓen 2027

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya mika fom din takararsa na shugaban kasa a jam’iyar APC inda kuma ya amince ya tsaya takara a karo na biyu tare da mataimakinsa Kashim Shettima a zaɓen shekarar 2027.

Ibrahim Masari mai bawa shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa ne ya sanar da haka a madadin shugaban kasar.

Masari ya mika fim din takarar Tinubu da Shettima a wurin wani gajeren taro da ya samu halartar shugabannin APC da aka gudanar otal ɗin Continental dake Abuja.

Mika fom din Masari ya yi ya tabbatar da cewa Tinubu zai cigaba da mulki tare da Kashim Shettima a zango na biyu matukar INEC ta ayyana su a matsayin wanda suka lashe zaɓen shugaban ƙasar da za a gudanar a 2027.

Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyar APC na daga cikin waɗanda suka halacci taron

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]