Rundunar Operation HADIN KAI ta ce dakarunta sun ceto karin mutane shida da aka sace a Jihar Borno yayin ci gaba da aikin bincike da ceto.
Sanarwar da jami’in yada labaran rundunar, Kyaftin Mohammed Goni, ya fitar ta bayyana cewa wadanda aka ceto sun hada da manya hudu da jarirai biyu. An ceto su ne a Talakawa da ke karamar hukumar Chibok.
Rahoton ya ce an sace mutanen ne tun watan Mayu daga yankin Mussa a karamar hukumar Askira/Uba.
Rundunar ta bayyana cewa an kai wadanda aka ceto wuri mai tsaro domin yi musu gwajin lafiya tare da ba su kulawar da ta dace kafin hada su da iyalansu.
Sanarwar ta kuma ce dakarun na ci gaba da bibiyar ’yan ta’addar da suka tsere, inda suka kwato harsasai guda hamsin na PKT da maharan suka bari a hanyarsu ta guduwa.
Sojoji Sun Ceto Karin Mutane Da Aka Sace a Borno

