Kotu Ta Yanke Wa Mutane 2 Hukuncin Kisa Kan Sace Jami’in NYSC A Ekiti


Babbar Kotun Jihar Ekiti ta yanke wa wasu mutane 2 hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsu da laifin sace wani jami’in Hukumar Yi Wa Ƙasa Hidima (NYSC), Omoboade Adesina.

Lamarin ya faru ne a ranar 22 ga Afrilu, 2022.

Waɗanda kotun ta samu da laifin sun haɗa da Ibrahim Abubakar da Abdullahi Abubakar, yayin da aka wanke mutum na uku mai suna Usman Abubakar saboda rashin isassun hujjojin da ke alaƙanta shi da laifin.

Jami’an Hukumar Tsaro ta DSS ne suka fara kama mutanen kafin a gurfanar da su a gaban kotu.

Babban Alƙalin jihar Ekiti, Lekan Ogunmoye, ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun tabbatar da zargin da ake yi wa mutanen biyu ba tare da wata shakka ba.

Kotun ta ce shaidu daga tantance waɗanda ake zargi da bayanan kiran waya sun haɗa mutanen biyu da laifin satar.

Daga nan ne kotun ta yanke musu hukuncin kisa ta hanyar rataya.

More from this stream

Recomended